- English
- King James KJV
- Complete Jewish CJB
- World English WEBM
- Berean Standard BSB
- American Standard ASV
- Geneva GNV
- Young's Literal YLT
- Douay-Rheims DRC
- International
- Shqip ALB
- العربية SVD
- বাংলা BN-IRV
- မြန်မာ Judson
- 简体文 CUV-S
- 繁體中文 CUV-T
- Čeština BKR
- Nederlands STVE
- Français LSG
- Deutsch SCH
- Ελληνικά Vamvas
- ગુજરાતી GU-IRV
- Hausa HCB
- עברית Hebrew
- हिन्दी HCV
- Magyar KAROLI
- Bahasa Indonesia INDO-TB
- Italiano Diodati
- 日本語 Kougo
- 한국어 Korean
- മലയാളം MAL
- मराठी MRCV
- Norsk DNB
- فارسی OPV
- Polski BG
- Português Almeida
- Română Cornilescu
- Русский Synodal
- Español RVG
- Kiswahili Neno
- Svenska SV1917
- Tagalog TAG-ADB
- தமிழ் TCV
- తెలుగు TSA
- ภาษาไทย THAI-KJV
- Українська Ohienko
- Tiếng Việt CADMAN
- Yorùbá YCB
Zabura66
Listen to this chapter
0:00
0:00
Kira ga dukan mutane su yi wa Allah sujada saboda ayyukansa
1
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Waƙa. Zabura. Ku yi sowa ta farin ciki ga Allah, dukan duniya!
2
Ku rera ɗaukaka ga sunansa; ku sa yabonsa yă zama da ɗaukaka!
3
Ku ce wa Allah, “Ayyukanka da banmamaki suke! Ikonka da girma yake har abokan gābanka suna durƙusa a gabanka.
4
Dukan duniya sun rusuna a gabanka suna rera yabo gare ka, suna rera yabo ga sunanka.” Sela
5
Ku zo ku ga abin da Allah ya yi, ayyukansa masu banmamaki a madadin mutum!
6
Ya juya teku zuwa busasshiyar ƙasa, sun wuce cikin ruwaye da ƙafa, ku zo, mu yi farin ciki a cikinsa.
7
Yana mulki har abada ta wurin ikonsa, idanunsa suna duban al’ummai, kada ’yan tawaye su tayar masa. Sela
Allah yana gwada jama’arsa yana kuma cetonsu
8
Ku yabi Allahnku, ya mutane, bari a ji ƙarar yabonsa;
9
ya adana rayukanmu ya kuma kiyaye ƙafafunmu daga santsi.
10
Gama kai, ya Allah, ka gwada mu; ka tace mu kamar azurfa.
11
Ka kawo mu cikin kurkuku ka kuma jibga kaya masu nauyi a bayanmu.
12
Ka bar mutane suka hau a kawunanmu; mun bi ta wuta da ruwa, amma ka kawo mu zuwa wurin yalwa.
Cika alkawuran godiya
13
Zan zo haikalinka da hadayun ƙonawa zan kuwa cika alkawurana gare ka,
14
alkawuran da leɓunana suka yi alkawari bakina kuma ya faɗa sa’ad da nake cikin wahala.
15
Zan miƙa kitsen dabbobi gare ka da kuma baye-baye na raguna; zan miƙa bijimai da awaki. Sela
Shaidar mutum game da amsar addu’a
16
Ku zo ku saurara, dukanku waɗanda suke tsoron Allah; bari in faɗa muku abin da ya yi mini.
17
Na yi kuka gare shi da bakina; yabonsa yana a harshena.
18
Da a ce na ji daɗin zunubi a zuciyata, da Ubangiji ba zai saurara ba;
19
amma tabbatacce Allah ya saurara ya kuma ji muryata a cikin addu’a.
20
Yabo ga Allah, wanda bai ƙi addu’ata ba ko yă janye ƙaunarsa daga gare ni!
Use ← → arrow keys to navigate
Settings
Reading Style
Typeface
Font Size px
Reading Width chars
Options
Study Note