- English
- King James KJV
- Complete Jewish CJB
- World English WEBM
- Berean Standard BSB
- American Standard ASV
- Geneva GNV
- Young's Literal YLT
- Douay-Rheims DRC
- International
- Shqip ALB
- العربية SVD
- বাংলা BN-IRV
- မြန်မာ Judson
- 简体文 CUV-S
- 繁體中文 CUV-T
- Čeština BKR
- Nederlands STVE
- Français LSG
- Deutsch SCH
- Ελληνικά Vamvas
- ગુજરાતી GU-IRV
- Hausa HCB
- עברית Hebrew
- हिन्दी HCV
- Magyar KAROLI
- Bahasa Indonesia INDO-TB
- Italiano Diodati
- 日本語 Kougo
- 한국어 Korean
- മലയാളം MAL
- मराठी MRCV
- Norsk DNB
- فارسی OPV
- Polski BG
- Português Almeida
- Română Cornilescu
- Русский Synodal
- Español RVG
- Kiswahili Neno
- Svenska SV1917
- Tagalog TAG-ADB
- தமிழ் TCV
- తెలుగు TSA
- ภาษาไทย THAI-KJV
- Українська Ohienko
- Tiếng Việt CADMAN
- Yorùbá YCB
Zabura116
Listen to this chapter
0:00
0:00
Sanarwar Ƙaunar Ubangiji
1
Ina ƙaunar Ubangiji, gama ya ji muryata; ya ji kukata ta neman jinƙai.
2
Domin ya juye kunnensa gare ni, zan kira gare shi muddin ina da rai.
Tunawa da Wahala da Addu’ar Ƙunci
3
Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni, wahalar kabari sun zo a kaina; na cika da wahala da ɓacin rai.
4
Sai na kira ga sunan Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji, ka cece ni!”
Shelar Jinƙai da Adalcin Allah
5
Ubangiji mai alheri ne da kuma mai adalci; Allahnmu yana cike da tausayi.
6
Ubangiji yana tsare masu tawali’u; sa’ad da nake cikin tsananin bukata, ya cece ni.
7
Ka kwantar da hankali, ya raina, gama Ubangiji mai alheri ne a gare ka.
8
Gama kai, ya Ubangiji, ka ceci raina daga mutuwa, idanuna daga hawaye, ƙafafuna daga tuntuɓe,
9
don in iya tafiya a gaban Ubangiji a ƙasar masu rai.
An Gwada Bangaskiya Cikin Wahala
10
Na gaskata, saboda haka na ce, “An azabtar da ni ƙwarai.”
11
Kuma cikin rikicewana na ce, “Dukan mutane maƙaryata ne.”
Aminci ga Alkawura da Bautar Jama’a
12
Yaya zan sāka wa Ubangiji saboda dukan alherinsa gare ni?
13
Zan daga kwaf na ceto in kuma kira ga sunan Ubangiji.
14
Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa.
15
Abu mai daraja a gaban Ubangiji shi ne mutuwar tsarkakansa.
16
Ya Ubangiji, da gaske ni bawanka ne; ni bawanka ne, ɗan baiwarka; ka ’yantar da ni daga sarƙoƙi.
17
Zan yi hadayar godiya gare ka in kuma kira bisa sunan Ubangiji.
18
Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa,
19
a filayen gidan Ubangiji, a tsakiyarki, ya Urushalima. Yabi Ubangiji.
Use ← → arrow keys to navigate
Settings
Reading Style
Typeface
Font Size px
Reading Width chars
Options
Study Note