Skip to content
Romawa 1:9

Romawa 1:9

Ana nuna aya 9 tare da mahallin da ke kewaye.
6
Ku ma kuna cikin waɗanda aka kira ku zama na Yesu Kiristi.
7
Wannan wasiƙa ce zuwa ga dukanku da kuke a Roma waɗanda Allah yake ƙauna, waɗanda kuma ya kira domin su zama tsarkaka. Alheri da salama daga Allah Ubanmu da kuma daga Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
8
Da farko, ina gode wa Allahna ta wurin Yesu Kiristi saboda ku duka, gama ana ba da labarin bangaskiyarku a ko’ina a duniya.
9
Allah, wanda nake bauta wa da dukan zuciyata cikin wa’azin bisharar Ɗansa, shi ne shaidata a kan yadda kullum ina tunawa da ku
10
cikin addu’o’ina a kowane lokaci; ina kuma addu’a cewa a ƙarshe in Allah ya yarda hanya za tă buɗe mini in zo wurinku.
11
Ina marmarin ganinku don in ba ku wata baiwar ruhaniya, don ku yi ƙarfi
12
wato, don ni da ku mu ƙarfafa juna ta wurin bangaskiyarmu.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options