Skip to content
Romawa 1:8-15

Romawa 1:8-15

8
Da farko, ina gode wa Allahna ta wurin Yesu Kiristi saboda ku duka, gama ana ba da labarin bangaskiyarku a ko’ina a duniya.
9
Allah, wanda nake bauta wa da dukan zuciyata cikin wa’azin bisharar Ɗansa, shi ne shaidata a kan yadda kullum ina tunawa da ku
10
cikin addu’o’ina a kowane lokaci; ina kuma addu’a cewa a ƙarshe in Allah ya yarda hanya za tă buɗe mini in zo wurinku.
11
Ina marmarin ganinku don in ba ku wata baiwar ruhaniya, don ku yi ƙarfi
12
wato, don ni da ku mu ƙarfafa juna ta wurin bangaskiyarmu.
13
Ina so ku sani ’yan’uwa cewa na yi shirin zuwa wurinku sau da dama (amma aka hana ni yin haka sai yanzu). Na so in zo domin in sami mutane wa Kiristi a cikinku, kamar yadda na yi a cikin sauran Al’ummai.
14
Ina da hakki ga Hellenawa da waɗanda ba Hellenawa ba, ga masu hikima da kuma marasa azanci.
15
Shi ya sa na yi himma sosai in yi muku wa’azin bishara ku ma da kuke a Roma.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options