Zabura 83:9-18
9
Ka yi musu abin da ka yi wa Midiyan, yadda ka yi wa Sisera da Yabin a kogin Kishon,
10
waɗanda suka hallaka a En Dor suka zama kamar juji a ƙasa.
11
Ka mai da manyansu kamar Oreb da Zeyib, dukan sarakunansu kamar Zeba da Zalmunna,
12
waɗanda suka ce, “Bari mu mallaki wuraren kiwon Allah.”
13
Ka mai da su kamar ɗan tsiron da kan karye, iska ta yi ta turawa, ya Allahna, kamar yayin da iska take hurawa,
14
kamar yadda wuta ke cin kurmi ko harshen wutar da take ci a kan duwatsu,
15
haka za ka kore su da iska mai ƙarfi ka kuma firgita su da guguwarka.
16
Ka rushe fuskokinsu da kunya don mutane su nemi sunanka, ya Ubangiji.
17
Bari su kasance cikin kunya da taƙaici; bari su hallaka cikin wulaƙanci.
18
Bari su san cewa kai, wanda sunansa ne Ubangiji, cewa kai kaɗai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya.
Settings