Zabura 83:13-18
13
Ka mai da su kamar ɗan tsiron da kan karye, iska ta yi ta turawa, ya Allahna, kamar yayin da iska take hurawa,
14
kamar yadda wuta ke cin kurmi ko harshen wutar da take ci a kan duwatsu,
15
haka za ka kore su da iska mai ƙarfi ka kuma firgita su da guguwarka.
16
Ka rushe fuskokinsu da kunya don mutane su nemi sunanka, ya Ubangiji.
17
Bari su kasance cikin kunya da taƙaici; bari su hallaka cikin wulaƙanci.
18
Bari su san cewa kai, wanda sunansa ne Ubangiji, cewa kai kaɗai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya.
Settings