Skip to content
Zabura 106:13-33

Zabura 106:13-33

13
Amma nan da nan suka manta abin da ya yi ba su kuwa jira shawararsa ba.
14
A cikin hamada suka bar sha’awarsu ta mamaye su a ƙasar da babu kome suka gwada Allah.
15
Sai ya ba su abin da suka roƙa, amma ya aika musu da muguwar cuta.
16
A sansani suka ji kishin Musa da kuma Haruna, wanda Ubangiji ya keɓe.
17
Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta binne iyalin Abiram.
18
Wuta ta ƙuno a cikin mabiyansu; harshen wuta ya cinye mugaye.
19
A Horeb suka yi ɗan maraƙi suka yi wa gunkin zubi daga ƙarfe sujada.
20
Suka sauke Ɗaukakarsu saboda siffar bijimi, wanda yake cin ciyawa.
21
Suka manta da Allahn da ya cece su, wanda ya aikata manyan abubuwa a Masar,
22
mu’ujizai a ƙasar Ham ayyukan banrazana a Jan Teku.
23
Don haka ya ce zai hallaka su, amma Musa, zaɓaɓɓensa, ya yi godo a gabansa don yă kau da hasalarsa daga hallaka su.
24
Sai suka rena ƙasa mai ni’ima; ba su gaskata alkawarinsa ba.
25
Suka yi gunaguni a tentunansu ba su kuwa yi biyayya da Ubangiji ba.
26
Saboda haka ya rantse musu ya kuma ɗaga hannu cewa zai sa su mutu a cikin hamada,
27
ya sa zuriyarsu su mutu a cikin al’ummai ya kuma watsar da su cikin dukan ƙasashe.
28
Suka haɗa kai da Ba’al-Feyor suka kuma ci hadayun da aka miƙa wa allolin da ba su da rai;
29
suka tsokane Ubangiji ya yi fushi ta wurin mugayen ayyukansu, sai annoba ta ɓarke a cikinsu.
30
Amma Finehas ya miƙe tsaye ya ɗauki mataki, sai annobar ta daina.
31
An ayana masa wannan a matsayin adalci har zamanai marar matuƙa masu zuwa.
32
A ruwan Meriba suka ba Ubangiji fushi, sai wahala ta zo wa Musa saboda su;
33
saboda sun yi tayarwa a kan Ruhun Allah, har mugayen kalmomi suka fito daga leɓunan Musa.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options