Skip to content
Zabura 106:6-12

Zabura 106:6-12

6
Mun yi zunubi, kamar yadda kakanninmu suka yi; mun yi ba daidai ba muka kuma aikata mugunta.
7
Sa’ad da kakanninmu suke a Masar, ba su damu da mu’ujizanka ba; ba su tuna yawan alheranka ba, suka kuma yi tayarwa a teku, Jan Teku.
8
Duk da haka ya cece su saboda sunansa, don yă sanar da ikonsa mai girma.
9
Ya tsawata wa Jan Teku, ya kuwa bushe; ya bi da su ta cikin zurfafa sai ka ce a hamada.
10
Ya cece su daga hannun maƙiyi; daga hannun abokin gāba ya fanshe su.
11
Ruwaye suka rufe abokan gābansu; babu ko ɗaya da ya tsira.
12
Sa’an nan suka gaskata alkawarinsa suka kuma rera yabonsa.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options