Skip to content
Zabura 106:34-46

Zabura 106:34-46

34
Ba su hallakar da mutanen yadda Ubangiji ya umarce su ba,
35
amma suka yi cuɗanya da al’ummai suka ɗauki al’adunsu.
36
Suka yi wa gumakansu sujada, waɗanda suka zama tarko gare su.
37
Suka miƙa ’ya’yansu maza hadaya ’yan matansu kuma ga aljanu.
38
Suka zub da jini marar laifi, jinin ’ya’yansu maza da mata, waɗanda suka miƙa hadaya ga gumakan Kan’ana, ƙasar kuwa ta ƙazantu ta wurin jininsu.
39
Suka ƙazantar da kansu ta wurin abin da suka yi; ta wurin ayyukansu suka yi karuwanci.
40
Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da mutanensa ya ji ƙyamar gādonsa.
41
Ya miƙa su ga al’ummai, maƙiyansu kuma suka yi mulki a kansu.
42
Abokan gābansu suka danne su suka sa su a ƙarƙashin ikonsu.
43
Sau da yawa ya cece su, amma sun nace su yi tawaye suka kuma lalace cikin zunubinsu.
44
Amma ya lura da wahalarsu sa’ad da ya ji kukansu;
45
saboda su ya tuna da alkawarinsa kuma daga yawan ƙaunarsa ya ji tausayi.
46
Ya sa aka ji tausayinsu a wurin dukan waɗanda suka kame su.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options