Skip to content
Markus 15:1-15

Markus 15:1-15

1
Da sassafe, sai manyan firistoci da dattawa, da malaman dokoki, da dukan Majalisa, suka yanke shawara. Suka daure Yesu, suka kai shi, suka miƙa shi ga Bilatus.
2
Bilatus ya yi tambaya ya ce, “Kai ne Sarkin Yahudawa?” Yesu ya amsa ya ce, “I, haka yake, kamar yadda ka faɗa.”
3
Manyan firistoci suka zarge shi a kan abubuwa da yawa.
4
Don haka Bilatus ya sāke tambayarsa ya ce, “Ba za ka amsa ba? Dubi abubuwa da yawa da suke zarginka da su.”
5
Amma har yanzu, Yesu bai ba da amsa ba, Bilatus ya yi mamaki.
6
Yanzu fa, al’ada ce a lokacin Bikin, a saki ɗan kurkuku guda wanda mutane suka roƙa.
7
Wani mutumin da ake kira Barabbas, yana a kurkuku, tare da waɗansu ’yan tawaye da suka yi kisankai a lokacin wani hargitsi.
8
Taron suka matso, suka ce roƙi Bilatus yă yi musu abin da ya saba yi.
9
Bilatus ya yi tambaya ya ce, “Kuna so in sakar muku Sarkin Yahudawa?”
10
Don ya san saboda sonkai ne manyan firistoci suka ba da Yesu a gare shi.
11
Amma manyan firistoci suka zuga taron su sa a saki Barabbas, a maimakon Yesu.
12
Bilatus ya tambaye su ya ce, “To, me zan yi da wanda kuke ce da shi, sarkin Yahudawa?”
13
Suka yi ihu, suka ce, “A gicciye shi!”
14
Bilatus ya yi tambaya ya ce, “Don me? Wane laifi ya yi?” Amma suka ƙara yin ihu suna cewa, “A gicciye shi!”
15
Don son yă faranta wa taron rai, sai Bilatus ya sakar musu Barabbas. Ya sa aka yi wa Yesu bulala, sa’an nan ya ba da shi a gicciye.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options