Skip to content
Luka 22:39-46

Yesu Ya Yi Addu’a a Dutsen Zaitun

Luka 22:39-46

Yesu Ya Yi Addu’a a Dutsen Zaitun

39
Yesu ya fita zuwa Dutsen Zaitun kamar yadda ya saba, almajiransa kuma suka bi shi.
40
Da ya kai wurin, sai ya ce musu, “Ku yi addu’a don kada ku fāɗi cikin jarraba.”
41
Sai ya janye daga wurinsu, misalin nisan jifa, ya durƙusa a ƙasa ya yi addu’a,
42
“Uba, in ka yarda, ka ɗauke mini wannan kwaf, amma ba nufina ba, sai dai naka.”
43
Wani mala’ika daga sama ya bayyana gare shi, ya ƙarfafa shi.
44
Domin tsananin azaba, sai ya ƙara himma cikin addu’a, zuffansa kuma na ɗigowa ƙasa kamar jini.
45
Da ya tashi daga addu’a, ya koma inda almajiransa suke, sai ya iske su suna barci, daga gajiyar baƙin ciki.
46
Ya tambaye su, “Don me kuke barci? Ku tashi ku yi addu’a, don kada ku fāɗi cikin jarraba.”

Nazarin nassin nan

Sharhi a kan nassin, ba aya ɗaya ba

Sauran wuraren da Nassi ya faɗi haka

  • Yohanna 12:27

    “Yanzu kuwa na damu, amma me zan ce? ‘Uba, ka cece ni daga wannan sa’a’? A’a, ai, saboda wannan dalili ne musamman na zo.
    daga aya ta 42
  • Yohanna 12:28

    Uba, ka ɗaukaka sunanka!” Sai wata murya ta fito daga sama ta ce, “Na riga na ɗaukaka shi, zan kuma ƙara ɗaukaka shi.”
    daga aya ta 42
  • Mattiyu 26:39

    Da ya yi gaba kaɗan, sai ya fāɗi a ƙasa, ya yi addu’a ya ce, “Ubana, in mai yiwuwa ne, a ɗauke mini wannan kwaf. Amma ba nufina ba, sai naka.”
    daga aya ta 41
  • Mattiyu 26:42

    Ya sāke tafiya sau na biyu, ya yi addu’a ya ce, “Ubana, in ba zai yiwu a ɗauke wannan kwaf ba sai na sha shi, to, bari a aikata nufinka.”
    daga aya ta 42
  • Markus 14:36

    Ya ce, “Ya Abba,Uba, kome mai yiwuwa ne a gare ka. Ka ɗauke mini wannan kwaf. Amma ba abin da nake so ba, sai dai abin da kake so.”
    daga aya ta 42
  • Zabura 40:8

    Ina sha’awar aikata nufinka, ya Allahna; dokar tana cikin zuciyata.”
    daga aya ta 42
  • Yohanna 18:11

    Sai Yesu ya umarce Bitrus ya ce, “Mai da takobinka kube! Ba zan sha kwaf da Uba ya ba ni ba?”
    daga aya ta 42
  • Mattiyu 20:22

    Yesu ya ce musu, “Ba ku san abin da kuke roƙo ba. Za ku iya sha daga kwaf da zan sha?” Suka amsa, “Za mu iya.”
    daga aya ta 42
  • Yohanna 5:30

    Ni kaɗai dai ba na iya yin kome, ina shari’a ne bisa ga abin da na ji. Shari’ata kuwa mai adalci ce. Gama ba na neman gamsar da kaina, sai dai in gamshi shi wanda ya aiko ni.
    daga aya ta 42
  • Mattiyu 4:11

    Sa’an nan Iblis ya bar shi, mala’iku kuwa suka zo suka yi masa hidima.
    daga aya ta 43
  • Yohanna 6:38

    Gama na sauko daga sama ba don in cika nufin kaina ba sai dai don in cika nufin shi wanda ya aiko ni.
    daga aya ta 42
  • Mattiyu 6:13

    Kada ka bari a kai mu cikin jarraba, amma ka cece mu daga mugun nan.’
    daga aya ta 40
All Luke Sites (Jerusalem)
All Luke Sites (Jerusalem) View full PDF
Luke 22:39-46, Luke 24:36-52
Luke 22:39-46, Luke 24:36-52 View full PDF
All Luke Sites (Levant)
All Luke Sites (Levant) View full PDF

Map © Biblica Open Bible Maps · CC BY-SA 4.0

Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options