Skip to content
Makoki 5:1-16

Makoki 5:1-16

1
Ka tuna, ya Ubangiji, abin da ya faru da mu; duba, ka ga kunyar da muka sha.
2
An ba wa baƙi gādonmu, gidajenmu kuma aka ba bare.
3
Mun zama marayu marasa ubanni, uwayenmu kamar gwauraye.
4
Dole mu sayi ruwan da muke sha; sai mun biya mu sami itace.
5
Masu fafararmu sun kusa kama mu; mun gaji kuma ba dama mu huta.
6
Mun miƙa kanmu ga Masar da Assuriya don mu sami isashen abinci.
7
Kakanninmu sun yi zunubi kuma ba sa nan yanzu, mu ne aka bari muna shan hukuncinsu.
8
Bayi suna mulki a kanmu, kuma ba wanda zai ’yantar da mu daga hannuwansu.
9
Muna samun burodi a bakin rayukanmu domin takobin da yake a jeji.
10
Fatar jikinmu ta yi zafi kamar murhu, muna jin zazzaɓi domin yunwa.
11
An yi wa mata fyaɗe a cikin Sihiyona, da kuma budurwai a cikin garuruwan Yahuda.
12
An rataye ’ya’yan sarakuna da hannuwansu; ba a ba wa dattawa girma.
13
Samari suna faman yin niƙa; yara kuma suna fama da ƙyar da nauyin kayan itace.
14
Dattawan sun bar ƙofar birnin, samari sun daina rera waƙa.
15
Farin ciki ya rabu da zuciyarmu; rayuwarmu ta zama makoki.
16
Rawani ya fāɗi daga kanmu. Kaiton mu gama mun yi zunubi!
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options