Makoki 5:4-10
4
Dole mu sayi ruwan da muke sha; sai mun biya mu sami itace.
5
Masu fafararmu sun kusa kama mu; mun gaji kuma ba dama mu huta.
6
Mun miƙa kanmu ga Masar da Assuriya don mu sami isashen abinci.
7
Kakanninmu sun yi zunubi kuma ba sa nan yanzu, mu ne aka bari muna shan hukuncinsu.
8
Bayi suna mulki a kanmu, kuma ba wanda zai ’yantar da mu daga hannuwansu.
9
Muna samun burodi a bakin rayukanmu domin takobin da yake a jeji.
10
Fatar jikinmu ta yi zafi kamar murhu, muna jin zazzaɓi domin yunwa.
Settings