Tsallake zuwa abun ciki
Makoki 3:1-15

Makoki 3:1-15

1
Ni ne mutumin da ya ga azaba ta wurin bulalar fushin Ubangiji.
2
Ya kore ni, ya sa na yi tafiya a cikin duhu maimakon a cikin haske;
3
ba shakka, ya juya mini baya, yana gāba da ni sau da sau, dukan yini.
4
Ya sa fatar jikina da naman jikina sun tsufa ya kuma karya ƙasusuwana.
5
Ya yi mini kwanton ɓauna ya kuma kewaye ni da baƙin ciki da kuma wahala.
6
Ya sa na zauna a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu da jimawa.
7
Ya kewaye ni yadda ba zan iya gudu ba; Ya daure ni da sarƙa mai nauyi.
8
Ko lokacin da nake kira don neman taimako, ba ya jin addu’ata.
9
Ya tare hanyata da tubula na duwatsu; ya sa hanyata ta karkace.
10
Kamar beyar da take a laɓe tana jira, kamar zaki a ɓoye,
11
ya janye ni daga kan hanya ya ɓatar da ni ya bar ni ba taimako.
12
Ya ja kwarinsa ya sa in zama abin baratarsa.
13
Ya harbi zuciyata da kibiyoyin kwarinsa.
14
Na zama abin dariya ga mutanena duka; suna yi mini ba’a cikin waƙa dukan yini.
15
Ya cika ni da kayan ɗaci ya gundure ni da abinci mai ɗaci.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options