Ayuba 29:1-11
1
Ayuba ya ci gaba da jawabinsa,
2
“Da ma ina nan lokacin da ya wuce baya can, kwanakin da Allah yake lura da ni,
3
lokacin da fitilarsa take haske a kaina na yi tafiya cikin duhu tare da haskensa.
4
Kwanakin da nake tasowa, lokacin da abokantakar Allah ta sa wa gidana albarka,
5
lokacin da Maɗaukaki yana tare da ni, kuma ’ya’yana suna kewaye da ni,
6
lokacin da ake zuba madara a inda nake takawa, duwatsu kuma suna ɓulɓulo mini man zaitun.
7
“Sa’ad da na je ƙofar birni na zauna a bainin jama’a,
8
matasan da suka gan ni sukan ja gefe tsofaffi kuma suka tashi tsaye;
9
sarakuna suka yi shiru suka rufe bakunansu da hannuwansu;
10
Muryar manya ta yi tsit harshensu ya manne a rufin bakunansu.
11
Duk wanda ya ji ni ya yaba mini waɗanda suka gan ni kuma sun amince da ni,
Settings