Tsallake zuwa abun ciki
Ayuba 24:13-17

Mugayen da suka yi tawaye ga haske

Ayuba 24:13-17
13
“Akwai waɗanda suke yi wa haske tawaye, waɗanda ba su san hanyoyinsa ba ko kuma ba su taɓa bin hanyoyinsa ba.
14
Sa’ad da hasken yini ya tafi, mai kisankai yakan tashi; yă je yă kashe matalauta da masu bukata; a cikin dare yake shigowa kamar ɓarawo.
15
Idanun mazinaci suna jiran yamma ta yi sosai; yana tunani cewa, ‘Ba wanda zai gan ni,’ sai kuma yă ɓoye fuskarsa.
16
Cikin duhu mutane suna fasa gidaje, amma da rana sukan kulle kansu; ba sa so wani abu yă haɗa su da haske.
17
Gama dukansu, duhu mai yawa shi ne safiyarsu; suna abokantaka da razanar duhu.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options