Tsallake zuwa abun ciki
Farawa 42:1-5

Yakubu ya aika ’ya’yansa Masar

Farawa 42:1-5
1
Sa’ad da Yaƙub ya sami labari cewa akwai hatsi a Masar, sai ya ce wa ’ya’yansa maza, “Don me kuke duban juna kawai?”
2
Ya ci gaba, “Na ji cewa akwai hatsi a Masar. Ku gangara can ku sayo mana, domin mu rayu kada mu mutu.”
3
Sai goma daga cikin ’yan’uwan Yusuf suka gangara don su saya hatsi daga Masar.
4
Amma Yaƙub bai aiki Benyamin, ɗan’uwan Yusuf tare da sauran ba, gama yana tsoro kada wani abu yă faru da shi.
5
Sai ’ya’yan Yaƙub suka isa Masar tare da sauran mutanen don sayen abinci, gama yunwar ta kai yankin Kan’ana ma.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options