Tsallake zuwa abun ciki
Fitowa 14:1-4

Allah ya nuna wa Isra’ila inda za su kafa sansani

Fitowa 14:1-4
1
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa,
2
“Ka faɗa wa Isra’ilawa, su juya su kafa sansani a Fi Hahirot, a tsakanin Migdol da teku. Za su kafa sansanin kai tsaye kusa da teku, wanda ya fuskanci Ba’al-Zafon.
3
Fir’auna zai yi tsammani, ‘Aha, Isra’ilawa sun rikice cikin ƙasar, hamada kuwa ta yimƙe su.’
4
Zan kuma taurare zuciyar Fir’auna, zai kuwa bi su. Na shirya wannan domin in nuna ɗaukakata a bisa Fir’auna da ƙungiyar sojansa. Bayan wannan, mutanen Masar za su sani ni ne Ubangiji.” Sai Isra’ilawa suka yi haka.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options