Skip to content
1 Tarihi 6:16-49

1 Tarihi 6:16-49

16
’Ya’yan Lawi maza su ne, Gershom, Kohat da Merari.
17
Waɗannan su ne sunayen ’ya’yan Gershom. Libni da Shimeyi.
18
’Ya’yan Kohat maza su ne, Amram, Izhar, Hebron da Uzziyel.
19
’Ya’yan Merari maza su ne, Mali da Mushi. Waɗannan suke gidajen Lawiyawan da aka jera bisa ga kakanninsu.
20
Na Gershom su ne, Libni, Yahat, Zimma,
21
Yowa, Iddo, Zera da Yeyaterai.
22
Zuriyar Kohat su ne, Amminadab, Kora, Assir,
23
Elkana, Ebiyasaf, Assir,
24
Tahat, Uriyel, Uzziya da Shawulu.
25
Zuriyar Elkana su ne, Amasai, Ahimot,
26
Elkana, Zofai, Nahat,
27
Eliyab Yeroham, Elkana da Sama’ila.
28
’Ya’yan Sama’ila maza su ne, Yowel ɗan fari da Abiya ɗa na biyu.
29
Zuriyar Merari su ne, Mali, Libni, Shimeyi, Uzza,
30
Shimeya, Haggiya da Asahiya.
31
Waɗannan su ne mutanen da Dawuda ya sa su lura da waƙa a cikin gidan Ubangiji bayan da aka kawo akwatin alkawari yă huta a can.
32
Suka yi hidima da waƙa a gaban tabanakul, Tentin Sujada, sai da Solomon ya gina haikalin Ubangiji a Urushalima. Suka yi ayyukansu bisa ga ƙa’idodin da aka shimfiɗa musu.
33
Ga mutanen da suka yi hidimar, tare da ’ya’yansu maza. Daga mutanen Kohat akwai, Heman, mawaƙi ɗan Yowel, ɗan Sama’ila,
34
ɗan Elkana, ɗan Yeroham, ɗan Eliyel, ɗan Towa,
35
ɗan Zuf, ɗan Elkana, ɗan Mahat, ɗan Amasai,
36
ɗan Elkana, ɗan Yowel, ɗan Azariya, ɗan Zefaniya
37
ɗan Tahat, ɗan Assir, ɗan Ebiyasaf, ɗan Kora,
38
ɗan Izhar, ɗan Kohat, ɗan Lawi, ɗan Isra’ila;
39
da kuma Asaf ’yan’uwan Heman, waɗanda suka yi hidima a hannun damansa. Asaf ɗan Berekiya, ɗan Shimeya,
40
ɗan Mika’ilu, ɗan Ba’asehiya, ɗan Malkiya,
41
ɗan Etni, ɗan Zera, ɗan Adahiya
42
ɗan Etan, ɗan Zimma, ɗan Shimeyi,
43
ɗan Yahat, ɗan Gershom, ɗan Lawi;
44
da kuma daga ’yan’uwansu, mutanen Merari, a hannun hagunsa. Etan ɗan Kishi, ɗan Abdi, ɗan Malluk,
45
ɗan Hashabiya, ɗan Amaziya, ɗan Hilkiya,
46
ɗan Amzi, ɗan Bani, ɗan Shemer,
47
ɗan Mali, ɗan Mushi, ɗan Merari, ɗan Lawi.
48
Aka ba ’yan’uwansu Lawiyawa dukan sauran ayyukan tabanakul, gidan Allah.
49
Amma Haruna da zuriyarsa su ne waɗanda suke miƙa hadayu a kan bagaden hadaya ta ƙonawa da kuma a kan bagaden turare haɗe da dukan abin da ake yi a Wuri Mafi Tsarki, suna yin kafara domin Isra’ila, bisa ga dukan abin da Musa bawan Allah ya umarta.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options