- English
- King James KJV
- Complete Jewish CJB
- World English WEBM
- Berean Standard BSB
- American Standard ASV
- Geneva GNV
- Young's Literal YLT
- Douay-Rheims DRC
- International
- Shqip ALB
- العربية SVD
- বাংলা BN-IRV
- မြန်မာ Judson
- 简体文 CUV-S
- 繁體中文 CUV-T
- Čeština BKR
- Nederlands STVE
- Français LSG
- Deutsch SCH
- Ελληνικά Vamvas
- ગુજરાતી GU-IRV
- Hausa HCB
- עברית Hebrew
- हिन्दी HCV
- Magyar KAROLI
- Bahasa Indonesia INDO-TB
- Italiano Diodati
- 日本語 Kougo
- 한국어 Korean
- മലയാളം MAL
- मराठी MRCV
- Norsk DNB
- فارسی OPV
- Polski BG
- Português Almeida
- Română Cornilescu
- Русский Synodal
- Español RVG
- Kiswahili Neno
- Svenska SV1917
- Tagalog TAG-ADB
- தமிழ் TCV
- తెలుగు TSA
- ภาษาไทย THAI-KJV
- Українська Ohienko
- Tiếng Việt CADMAN
- Yorùbá YCB
Zabura25
Listen to this chapter
0:00
0:00
Addu’ar neman ja-gora da kāriya
1
Ta Dawuda. A gare ka Ya Ubangiji, na miƙa raina.
2
A gare ka na dogara, ya Allahna. Kada ka bari in sha kunya, ko ka bar abokan gābana su yi nasara a kaina.
3
Ba wanda yake sa bege a gare ka da zai taɓa shan kunya, amma za su sha kunya su da suke tayarwa babu dalili.
4
Ka nuna mini hanyoyinka, ya Ubangiji, ka koya mini hanyoyinka;
5
ka bi da ni cikin gaskiyarka ka kuma koya mini, gama kai ne Allah Mai cetona, kuma begena yana a kanka dukan yini.
6
Ka tuna, ya Ubangiji da jinƙai da kuma ƙaunarka mai girma, gama suna nan tun dā.
7
Kada ka tuna da zunuban ƙuruciyata da kuma hanyoyin tawayena; bisa ga ƙaunarka ka tuna da ni, gama kai nagari ne, ya Ubangiji.
Nagartar Allah tana ja-gorar masu tawali’u
8
Ubangiji nagari da mai adalci ne; saboda haka yakan koyar da masu zunubi a hanyoyinsa.
9
Yakan bi da masu tawali’u cikin abin da yake daidai ya kuma koyar da su hanyoyinsa.
10
Dukan hanyoyin Ubangiji ƙaunatattu ne da kuma aminci ga waɗanda suke kiyaye abin da alkawari ya bukaci.
11
Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka gafarta laifina, ko da yake mai girma ne.
Albarkar tsoron UBANGIJI
12
To wane ne mai tsoron Ubangiji? Zai koyar da shi a hanyar da ya zaɓa masa.
13
Zai ci kwanakinsa a wadace, kuma zuriyarsa za su gāji ƙasar.
14
Ubangiji yakan amince da waɗanda suke tsoronsa; yakan sa su san alkawarinsa.
15
Idanuna kullum suna a kan Ubangiji, gama shi ne kaɗai zai kuɓutar da ƙafafuna daga tarko.
Roƙon ceto da gaske
16
Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, gama na kaɗaice ina kuma wahala.
17
Damuwoyin zuciyata sun ninka; ka ’yantar da ni daga wahalata.
18
Ka dubi wahalata da kuma azabata ka ɗauke mini dukan zunubaina.
19
Dubi yadda abokan gābana sun ƙaru da kuma yadda suka ƙara ƙina!
20
Ka tsare raina ka kuma kuɓutar da ni; kada ka bari in sha kunya, gama na nemi mafaka daga gare ka.
21
Bari mutunci da adalci su tsare ni, domin begena yana a kanka.
22
Ka fanshi Isra’ila, ya Allah, daga dukan wahalarsu!
Use ← → arrow keys to navigate
Settings
Reading Style
Typeface
Font Size px
Reading Width chars
Options
Study Note