Skip to content
Zabura 60:6-12

Zabura 60:6-12

6
Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Da nasara zan rarraba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
7
Gileyad nawa ne, Manasse kuma nawa ne; Efraim shi ne hular kwanona, Yahuda kuma sandar mulkina.
8
Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirarin nasara.”
9
Wa zai kawo ni birnin katanga? Wa zai bishe ni zuwa Edom?
10
Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
11
Ka ba mu gudummawa a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
12
Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattake abokan gābanmu.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options