9
Wa zai kawo ni birnin katanga? Wa zai bishe ni zuwa Edom?
10
Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
11
Ka ba mu gudummawa a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
12
Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattake abokan gābanmu.