Zabura 61:1-4
1
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Ta Dawuda. Ka ji kukata, ya Allah; ka saurari addu’ata.
2
Daga iyakar duniya na yi kira gare ka, na yi kira yayinda zuciyata ta karai; ka bishe ni zuwa dutsen da ya fi ni tsayi.
3
Gama kai ne mafakata, hasumiya mai ƙarfi gāba da maƙiyi.
4
Ina marmari in zauna a tentinka har abada in sami mafaka a cikin inuwar fikafikanka. Sela
Settings