Skip to content
Zabura 60:1-5

Zabura 60:1-5

1
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin Alkawari.” Wani miktam ta Dawuda. Don koyarwa. Sa’ad da ya yaƙi Aram-Naharayim da Aram-Zoba, da kuma sa’ad da Yowab ya dawo ya bugi mutanen Edom dubu goma sha biyu a Kwarin Gishiri. Ka ki mu, ya Allah, ka kuma fashe kāriyarmu; ka yi fushi da mu, yanzu ka mai da mu!
2
Ka girgiza ƙasar ka kuma tsaga ta; ka daure karayarta, gama tana rawa.
3
Ka nuna wa mutanenka lokutan wahala; ka ba mu ruwan inabin da ya sa muka bugu.
4
Amma ga waɗanda suke tsoronka, ka ɗaga tuta don a buɗe gāba da baka. Sela
5
Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options