Skip to content
Zabura 59:14-17

Zabura 59:14-17

14
Sukan dawo da yamma, suna wage haƙora kamar karnuka, suna yawo a birni.
15
Suna ta yawo neman abinci su kuwa yi haushi in ba su ƙoshi ba.
16
Amma zan rera game da ƙarfinka, da safe zan rera game da ƙaunarka; gama kai ne mafakata, kagarata a lokacin wahala.
17
Ya ƙarfina, na rera yabo gare ka; kai, ya Allah, kai ne kagarata, Allah mai ƙaunata.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options