Skip to content
Zabura 50:7-13

Zabura 50:7-13

7
“Ku ji, ya mutanena, zan kuwa yi magana, Ya Isra’ila, zan kuwa ba da shaida a kanku. Ni ne Allah, Allahnku.
8
Ba na tsawata muku saboda hadayunku ko kuwa hadayunku na ƙonawa, waɗanda kuka taɓa kawo a gabana.
9
Ba na bukatan bijimi daga turkenku ko awaki daga garkunanku,
10
gama kowace dabbar kurmi nawa ne, da kuma shanu a kan dubban tuddai.
11
Na san kowane tsuntsun da yake a duwatsu kuma halittun filaye nawa ne.
12
Da a ce ina jin yunwa ai, ba sai na faɗa muku ba, gama duniyar nawa ne, da kome da yake cikinta.
13
Ina cin naman bijimai ne ko ina shan jinin awaki ne?
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options