Zabura 50:1-6
1
Zabura ta Asaf. Maɗaukaki, Allah, Ubangiji, ya yi magana ya kuma kira duniya daga fitowar rana zuwa inda take fāɗuwa.
2
Daga Sihiyona, cikakkiya a kyau, Allah na haskakawa.
3
Allahnmu yana zuwa ba kuwa zai yi shiru ba; wuta mai cinyewa a gabansa, babban hadari kuma ya kewaye shi.
4
Ya kira sammai da suke bisa, da duniya, don yă shari’anta mutanensa.
5
“Ku tattara mini shafaffuna, waɗanda suka yi alkawari da ni ta wurin hadaya.”
6
Sammai kuwa sun yi shelar adalcinsa gama Allah kansa alƙali ne. Sela
Settings