Zabura 44:9-14
9
Amma yanzu ka ƙi mu ka kuma ƙasƙantar da mu; ba ka ƙara fita tare da mayaƙanmu.
10
Ka sa muka gudu a gaban abokin gāba, kuma abokan gābanmu suka washe mu.
11
Ka ba da mu a cinye kamar tumaki ka kuma watsar da mu a cikin al’ummai.
12
Ka sayar da mutanenka a kuɗin da bai taka ƙara ya karye ba babu wata riba daga sayar da su da ka yi.
13
Ka mai da mu abin dariya ga maƙwabtanmu, abin dariya da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
14
Ka sa muka zama abin ba’a a cikin al’ummai; mutanen suna kaɗa mana kai.
Settings