Skip to content
Zabura 44:1-8

Zabura 44:1-8

1
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta ’ya’yan Kora maza. Maskil ne. Mun ji da kunnuwanmu, ya Allah; kakanninmu sun faɗa mana abin da ka aikata a kwanakinsu, tun dā can.
2
Da hannunka ka kori al’ummai ka kuma dasa kakanninmu; ka ragargaza mutanen ka kuma sa kakanninmu suka haɓaka.
3
Ba da takobinsu ba ne suka ci ƙasar, ba kuwa ƙarfin hannunsu ne ya ba su nasara ba; hannun damanka ne, ƙarfin hannunka, da kuma hasken fuskarka, gama ka ƙaunace su.
4
Kai ne Sarkina da kuma Allahna, wanda ya ba da nasarori wa Yaƙub.
5
Ta wurinka mun tura abokan gābanmu baya; ta wurin sunanka muka tattake maƙiyanmu.
6
Ba na dogara ga bakana, takobina ba ya kawo nasara;
7
amma kana ba mu nasara a kan abokan gābanmu, ka sa abokan gābanmu suka sha kunya.
8
A cikin Allah muke fariyarmu dukan yini, kuma za mu yabi sunanka har abada. Sela
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options