Skip to content
Zabura 137:1-6

Zabura 137:1-6

1
A bakin kogunan Babilon muka zauna muka yi kuka sa’ad da muka tuna da Sihiyona.
2
A can a kan rassan itatuwa muka rataye garayunmu,
3
gama a can masu kamunmu suka sa mu yi waƙoƙi, masu ba mu azaba suka nema waƙoƙin farin ciki; suka ce, “Ku rera mana ɗaya daga cikin waƙoƙin Sihiyona!”
4
Yaya za mu rera waƙoƙin Ubangiji a baƙuwar ƙasa?
5
In na manta da ke, ya Urushalima, bari hannuna na dama manta da iyawarsa.
6
Bari harshena yă manne wa rufin bakina in ban tuna da ke ba, in ban so Urushalima farin cikin mafi girma ba.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 90 chars

Options