Zabura 137:1-4
1
A bakin kogunan Babilon muka zauna muka yi kuka sa’ad da muka tuna da Sihiyona.
2
A can a kan rassan itatuwa muka rataye garayunmu,
3
gama a can masu kamunmu suka sa mu yi waƙoƙi, masu ba mu azaba suka nema waƙoƙin farin ciki; suka ce, “Ku rera mana ɗaya daga cikin waƙoƙin Sihiyona!”
4
Yaya za mu rera waƙoƙin Ubangiji a baƙuwar ƙasa?
Settings