Tsallake zuwa abun ciki
Zabura 106:1-5

Gabatarwa: Kira ga yabo da addu’a

Zabura 106:1-5
1
Yabi Ubangiji. Yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2
Wane ne zai furta manyan ayyukan Ubangiji ko yă furta cikakken yabonsa?
3
Masu albarka ne waɗanda suke yin adalci, waɗanda kullum suke yin abin da yake daidai.
4
Ka tuna da ni, ya Ubangiji, sa’ad da ka nuna alheri ga mutanenka, ka zo ka taimake ni sa’ad da ka cece su,
5
don in ji daɗin nasarar zaɓaɓɓunka, don in sami rabo cikin farin cikin al’ummarka in kuma shiga gādonka cikin yin yabo.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options