Skip to content
Zabura 105:37-45

Zabura 105:37-45

37
Ya fitar da Isra’ila, ɗauke da azurfa da zinariya, kuma daga cikin kabilansu babu wani da ya kāsa.
38
Masar ta yi murna sa’ad da suka tafi, saboda tsoron Isra’ila ya fāɗo musu.
39
Ya shimfiɗa girgije kamar mayafi, da kuma wuta don ta ba su haske da dare.
40
Suka roƙa, ya kuwa ba su makware ya kuma ƙosar da su da abinci daga sama.
41
Ya buɗe dutse, sai ruwa ya ɓulɓulo, kamar kogi ya gudu zuwa cikin hamada.
42
Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki da ya ba wa bawansa Ibrahim.
43
Ya fitar da mutanensa da farin ciki, zaɓaɓɓunsa da sowa ta farin ciki;
44
ya ba su ƙasashen al’ummai, suka kuma sami gādon abin da waɗansu sun sha wahala a kai,
45
don su kiyaye farillansa su kuma kiyaye dokokinsa. Yabo ga Ubangiji.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options