মূল বিষয়বস্তুতে যান
Karin Magana 5:15-23

Karin Magana 5:15-23

15
Ku sha ruwa daga tankinku, ruwa mai gudu daga rijiyarku.
16
In maɓulɓulanku suka cika suna malala har waje, rafuffukan ruwanku a dandalin jama’a?
17
Bari su zama naka kaɗai, don kada ka raba da baƙi.
18
Bari maɓulɓulanka ya zama mai albarka, bari kuma ka yi farin ciki da matar ƙuruciyarka.
19
Ƙaunatacciyar mariri, barewa mai kyan gani, bari mamanta su ishe ka kullum, bari ƙaunarta ta ɗauke hankalinka kullum.
20
Ɗana, me ya sa za ka bari mazinaciya ta ɗauke maka hankali? Don me za ka rungume matar wani?
21
Gama hanyar mutum a bayyane take a gaban Ubangiji, yana kuma lura da dukan hanyoyinsa.
22
Ayyukan mugunta na mugun mutum tarko ne gare shi; igiyoyin zunubinsa za su daure shi kankan.
23
Zai mutu saboda rashin ɗa’a yawan wawancinsa zai sa yă kauce.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options