Skip to content
Karin Magana 20:13-19

Karin Magana 20:13-19

13
Kada ka so barci in ba haka ba za ka talauce; ka zauna a faɗake za ka kuwa kasance da sauran abinci.
14
“Kai, ya yi tsada, ya yi tsada!” In ji mai saya; sa’ad da ya tafi yana taƙama a kan ya iya ciniki.
15
Zinariya akwai ta, lu’ulu’u kuma ga shi a yalwace, amma leɓunan da suke magana da sani suna da wuyan samu kamar duwatsu masu daraja.
16
A karɓi rigunan wanda ya ɗauki lamunin baƙo; a riƙe shi jingina in ya yi shi don mace marar aminci.
17
Abincin da aka samu ta hanyar zamba yakan zama da daɗi, amma mutum zai ƙarasa da baki cike da yashi.
18
Ka yi shirye-shirye ta wurin neman shawara; in kana yaƙi, ka sami bishewa.
19
Mai gulma yakan lalace yarda; saboda haka ka guji mutum mai yawan surutu.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options