Karin Magana 20:20-25
20
In mutum ya zargi mahaifinsa ko mahaifiyarsa, fitilarsa za tă mutu a tsakiyar duhu.
21
Gādon da aka samu da sauri a farkon farawa ba zai zama mai albarka a ƙarshe ba.
22
Kada ka ce, “Zan rama wannan abin da aka yi mini!” Ka dogara ga Ubangiji, zai kuwa fisshe ka.
23
Ubangiji ya ƙi ma’aunin da ba daidai ba, da kuma magwajin da ba su gamshe shi ba.
24
Ubangiji ne yake bi da matakan mutum, Ta yaya wani zai fahimci hanyarsa?
25
Tarko ne ga mutum ya keɓe wani abu da ba tunani daga baya kuma ya yi la’akari da alkawarinsa.
Settings