Skip to content
Karin Magana 20:26-30

Karin Magana 20:26-30

26
Sarki mai hikima yakan gane mugunta; ya hukunta su ba tausayi.
27
Fitilar Ubangiji kan bincika zuciyar mutum takan bincika lamirinsa.
28
Ƙauna da aminci kan kiyaye sarki lafiya; ta wurin ƙauna sarautarsa za tă zauna a kafe.
29
Ɗaukakar matasa maza ita ce ƙarfinsu, furfura ita ce darajar tsofaffi.
30
Naushi da rauni kan share mugunta, dūka kuma kan tsabtacce lamiri.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options