Karin Magana 21:1-8
1
A hannun Ubangiji zuciyar sarki kamar ruwan rafi ne wanda yake bi da shi duk inda ya so.
2
Mutum zai yi tunani hanyoyinsa daidai suke, amma Ubangiji yakan auna zuciya.
3
Yin abin da yake daidai da kuma nagari Ubangiji ya fi yarda da shi fiye da hadaya.
4
Girmankai da fariya, su ne fitilar mugaye, wannan kuwa zunubi ne!
5
Shirye-shiryen mai aiki tuƙuru kan kai ga riba in kuwa ka cika gaggawa zai kai ga talauci.
6
Dukiyar da aka samu ta wurin harshe mai yin ƙarya tarin tururi ne da kuma mugun tarko.
7
Rikicin mugaye zai yi gāba da su, gama sun ƙi su yi abin da yake daidai.
8
Hanyar mai laifi karkatacciya ce, amma halin marar laifi sukan aikata gaskiya.
Settings