Skip to content
Karin Magana 20:9-12

Karin Magana 20:9-12

9
Wa zai iya cewa, “Na kiyaye zuciyata da tsarki; ni mai tsabta ne marar zunubi kuma”?
10
Ma’auni marar gaskiya da magwajin da ba daidai ba, Ubangiji ya ƙi su duka.
11
Akan san ƙananan yara ta ayyukansu, ana iya sani ko rayuwarsu amintattu ne, mai nagarta.
12
Kunnuwan da suke ji da kuma idanun da suke gani, Ubangiji ne ya yi su duka.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options