Tsallake zuwa abun ciki
Obadiya 1:1-4

An Bayyana Hukunci a kan Edom

Obadiya 1:1-4
1
Wahayin Obadiya. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce a kan Edom. Mun ji saƙo daga wurin Ubangiji cewa, An aiki jakada zuwa ga al’ummai yă faɗa musu cewa, “Ku tashi, mu tafi mu yi yaƙi da ita.”
2
“Duba, zan maishe ki ƙarama a cikin al’ummai; za a rena ki ƙwarai.
3
Fariyar zuciyarki ta yaudare ki, ke da kike zama can bisa duwatsu kika kuma yi gidanki a kan ƙwanƙoli, ke da kike ce wa kanki, ‘Wa zai iya saukar da ni ƙasa?’
4
Ko da yake kina firiya kamar gaggafa kin kuma yi sheƙarki a can cikin taurari, daga can zan saukar da ke,” in ji Ubangiji.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options