Tsallake zuwa abun ciki
Ƙidaya 31:1-6

Ubangiji ya umarci ɗaukar fansa a kan Midiyawa

Ƙidaya 31:1-6
1
Ubangiji ya ce wa Musa,
2
“Ka ɗaukar wa Isra’ilawa fansa, a kan Midiyawa. Bayan wannan za ka mutu, a kuwa tara ka ga mutanenka.”
3
Saboda haka Musa ya ce wa mutane, “Ku shirya waɗansu daga cikin mazanku, su tafi su yi yaƙi da Midiyawa don su ɗaukar wa Ubangiji fansa a kansu.”
4
Ku aiki maza dubu ɗaya daga kowace kabilar Isra’ila.
5
Saboda haka aka samo mayaƙa dubu goma sha biyu shiryayyu don yaƙi, maza dubu ɗaya daga kowace kabilar Isra’ila.
6
Musa ya aike su zuwa yaƙi, dubu ɗaya daga kowace kabila, tare da Finehas ɗan Eleyazar, firist, wanda ya ɗauki kayayyaki daga wuri mai tsarki da ƙahoni don kiran yaƙi.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options