Tsallake zuwa abun ciki
Mattiyu 4:12-17

Yesu ya fara hidimarsa a Galili

Mattiyu 4:12-17
12
Da Yesu ya ji labari cewa an kulle Yohanna a kurkuku, sai ya koma zuwa Galili.
13
Ya bar Nazaret, ya je ya zauna a Kafarnahum, wadda take a bakin tafki wajen Zebulun da Naftali
14
don a cika abin da aka faɗa ta bakin annabi Ishaya cewa,
15
“Ƙasar Zebulun da ƙasar Naftali, da kuke a hanyar zuwa tekun Galili, a ƙetaren Urdun, wannan yankin Galili ta Al’ummai,
16
mutanen da suke zama cikin duhu sun ga babban haske; haske kuma ya haskaka a kan waɗanda suke zama a inuwar mutuwa.”
17
Tun daga wannan lokaci, Yesu ya fara wa’azi yana cewa, “Ku tuba, gama mulkin sama ya yi kusa.”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options