Skip to content
Mattiyu 24:15-22

Mattiyu 24:15-22

15
“Saboda haka sa’ad da kuka ga ‘abin ƙyama mai kawo hallaka,’wanda annabi Daniyel ya yi magana a kai, yana tsaye a tsattsarkan wuri (mai karatu yă gane),
16
to, sai waɗanda suke cikin Yahudiya, su gudu zuwa cikin duwatsu.
17
Kada wani da yake a kan rufin gidansa, yă sauko don ɗaukar wani abu a gida.
18
Kada wani da yake gona kuma yă komo don ɗaukar rigarsa.
19
Kaiton mata masu ciki da mata masu renon ’ya’ya a waɗancan kwanakin!
20
Ku yi addu’a, kada gudunku yă zama a lokacin sanyi ko a ranar Asabbaci.
21
Gama a lokacin za a yi wata matsananciyar wahala, wadda ba a taɓa yi ba tun farkon duniya har ya zuwa yanzu ba kuwa za a ƙara yi ba.
22
“Da ba don an taƙaita kwanakin nan ba, da babu wani da zai tsira, amma saboda zaɓaɓɓun nan, za a taƙaita kwanakin.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options