Skip to content
Yoshuwa 19:25-30

Yoshuwa 19:25-30

25
Ƙasarsu gādonsu ta haɗa da, Helkat, Hali, Beten, Akshaf,
26
Allammelek, Amad da Mishal. A arewanci kuma iyakar ta taɓa Karmel da Shihor Libnat.
27
Sai ta yi gabas zuwa Bet-Dagon, ta taɓa Zebulun da kuma Kwarin Ifta El, ta wuce arewa zuwa Bet-Emek da Neyiyel, ta wuce Kabul a hagu,
28
ta kai Abdon, Rehob, Hammon da Kana, har zuwa Sidon Babba.
29
Daga nan iyakar ta juya baya zuwa Rama, ta bi ta birnin nan mai katanga na Taya, ta juya ta nufi Hosa, sa’an nan ta ɓulla ta Bahar Rum cikin yankin Akzib,
30
Umma, Afek da Rehob. Garuruwa ashirin da biyu ke nan da ƙauyukansu.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options