Tsallake zuwa abun ciki
Yohanna 9:1-7

Warkar da Mutumin da Aka Haifa Makaho

Yohanna 9:1-7
1
Da Yesu yana tafiya, sai ya ga wani mutum wanda aka haifa makaho.
2
Sai almajiransa suka tambaye shi suka ce, “Rabbi, wane ne ya yi zunubi, mutumin ne, ko iyayensa, da ya sa aka haife shi makaho?”
3
Sai Yesu ya ce, “Ba don mutumin ko iyayensa sun yi zunubi ne ba, sai dai don a bayyana aikin Allah ne a rayuwarsa.
4
Muddin da sauran rana, dole mu yi aikin wanda ya aiko ni. Dare yana zuwa, sa’ad da ba wanda zai iya yin aiki.
5
Yayinda ina a cikin duniya, ni ne hasken duniya.”
6
Bayan ya faɗi haka, sai ya tofa miyau a ƙasa, ya kwaɓa laka da miyau ɗin, ya kuma shafa a idanun mutumin.
7
Ya ce masa, “Je ka, ka wanke a Tafkin Silowam” (kalman nan tana nufin “Aikakke”). Saboda haka mutumin ya tafi ya wanke, ya kuma dawo gida yana gani.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options