Skip to content
Yohanna 9:8-12

Yohanna 9:8-12

8
Maƙwabta da waɗanda suka saba ganinsa dā yana bara, suka ce, “Kai, ba wannan mutum ne ya saba zama yana bara ba?”
9
Waɗansu suka ce shi mana. Waɗansu kuwa suka ce, “A’a, ya dai yi kama da shi.” Amma shi ɗin ya ce, “Ƙwarai kuwa ni ne.”
10
Sai suka ce, “To, yaya aka yi idanunka suka buɗe?”
11
Ya amsa ya ce, “Mutumin da ake kira Yesu ne ya kwaɓa laka ya shafa mini a idanu. Ya ce mini in je Silowam in wanke. Na kuwa tafi, na wanke, sai na sami ganin gari.”
12
Suka tambaye shi suka ce, “Ina mutumin yake?” Ya ce, “Ban sani ba.”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options