Skip to content
Yohanna 7:47-52

Yohanna 7:47-52

47
Sai Farisiyawa suka amsa cikin fushi suka ce, “Af, kuna nufi har da ku ma ya ruɗe ku ke nan?
48
Akwai wani daga cikin masu mulki ko cikin Farisiyawan da ya gaskata da shi?
49
A’a! Sai dai wannan taron da ba su san kome game da Doka ba, la’anannu ne.”
50
Nikodimus, wanda ya je wurin Yesu dā, wanda kuma yake ɗayansu ya ce,
51
“Ashe, dokarmu takan hukunta mutum ba tare da an fara ji daga bakinsa game da abin da yake yi ba?”
52
Sai suka amsa suka ce, “Kai ma daga Galili ne? Bincika ka gani, za ka iske cewa ba annabin da zai fito daga Galili.”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options