Tsallake zuwa abun ciki
Ayuba 5:8-16

Elifaz ya ba da shawarar neman Allah

Ayuba 5:8-16
8
“Amma da a ce ni ne, da zan roƙi Allah; zan gaya masa damuwata.
9
Yana yin abubuwan al’ajabi waɗanda ba a ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a ƙirgawa.
10
Yana zuba ruwan sama a ƙasa; yana zuba ruwa a gonaki.
11
Yana ɗaukaka masu sauƙinkai, yana kāre waɗanda suke makoki.
12
Yana dagula shirye-shiryen masu wayo don kada su yi nasara cikin abubuwan da suke shirin yi.
13
Yana kama masu wayo cikin wayonsu, yana kawar da shirye-shiryensu ba za su yi nasara ba.
14
Da rana sukan yi karo da duhu; da rana ma suna lallube kamar a duhun dare suke.
15
Yana ceton matalauta daga takobin da za tă kashe su da shi; yana cetonsu daga hannun waɗanda suka fi su ƙarfi.
16
Saboda haka matalauta suna da bege, rashin gaskiya kuma ta yi shiru.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options