Ayuba 5:1-7
1
“Ka yi kira in kana so, amma wa zai amsa maka? Wurin waɗanne tsarkaka za ka juya?
2
Fushi yana kashe wawa, ƙyashi kuma yana kashe marar azanci.
3
Ni ma na ga wawa yana cin gaba, amma nan da nan gidansa ya zama la’ananne.
4
’Ya’yansa suna cikin hatsari, ba wanda zai tsaya musu a gaban alƙali,
5
mayunwata sun kwashe girbinsa, har abubuwan da suke cikin ƙaya, masu jin ƙishirwa kuma suna zuba ido ga dukiyarsa.
6
Gama ba daga cikin ƙasa wahala take fitowa ba, ko kuma bala’i daga ƙasa.
7
Duk da haka an haifi mutum don wahala ne, kamar yadda ba shakka tartsatsin wuta yake tashi.
Settings