Ayuba 5:8-16
8
“Amma da a ce ni ne, da zan roƙi Allah; zan gaya masa damuwata.
9
Yana yin abubuwan al’ajabi waɗanda ba a ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a ƙirgawa.
10
Yana zuba ruwan sama a ƙasa; yana zuba ruwa a gonaki.
11
Yana ɗaukaka masu sauƙinkai, yana kāre waɗanda suke makoki.
12
Yana dagula shirye-shiryen masu wayo don kada su yi nasara cikin abubuwan da suke shirin yi.
13
Yana kama masu wayo cikin wayonsu, yana kawar da shirye-shiryensu ba za su yi nasara ba.
14
Da rana sukan yi karo da duhu; da rana ma suna lallube kamar a duhun dare suke.
15
Yana ceton matalauta daga takobin da za tă kashe su da shi; yana cetonsu daga hannun waɗanda suka fi su ƙarfi.
16
Saboda haka matalauta suna da bege, rashin gaskiya kuma ta yi shiru.
Settings